Rundunar yan Sandan Nigeria ta gano masu shirya zanga-zanga irin ta Kenya a ƙasar

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Sufeto Janar na ‘yan sandan Najeriya, Kayode Egbetokun, ya ce bayanan sirri da rundunar ta samu sun nuna cewa akwai wasu yan kasashen waje da ke da hannu wajen shirya zanga-zangar da za a yi a fadin kasar.

Da yake jawabi ga manema labarai a Abuja ranar juma’a,, Egbetokun ya bukaci daukacin ‘yan Najeriya da su yi taka-tsan-tsan tare da yin tunani sosai kafin su shiga zanga-zangar.

Talla
Talla

Egbetokun ya ce, “Mun sanya ido kan abun dake faruwa game da shirin yin zanga-zangar. Mun gano wasu kungiyoyi na kira da ayi zanga-zangar tarzoma, suna bukatar ayi irin abun da aka yi a kasar Kenya na baya-bayan nan, wasu kuma suna ba da shawarar yin zanga-zangar lumana.

Zanga-zanga: Abubuwan da Tinubu ya fadawa Malamai da Sarakuna a ganawarsa da su

Babu shakka akwai mutanen da su burinsu a yi zanga-zangar lumana ba tare da tashin hankali ba, amma yace damuwarsu ita ce a Nigeria ba a taba yin zanga-zanga ba tare da an sami matsala ba, Kuma tabbatar mun gano akwai yan kasashen waje da suke tunzura mutane su yi zanga-zangar ba tare da la’akari da illolin ta ba.nuna damuwa game da gaskiyarsu.

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta bukaci dukkan ‘yan Najeriya da su yi taka-tsan-tsan kuma su yi tunani sosaiRundunar yan Sandan Nigeria ta gano masu shirya zanga-zanga irin ta Kenya a ƙasar  kafin su shiga wata zanga-zanga.”

Punch

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Sanata Kawu Sumaila ya kawo aikin sama da Naira Biliyan 120 Kano

Daga Isa Ahmad Getso   Sanatan Kano ta kudu Sulaiman Abdulrahman...

Inganta ilimi: Gwamnan Kano ya zama Gwarzon Shekarar 2024

Daga Rahama Umar Kwaru   Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Yanzu-yanzu: Sarki Sanusi ya nada sabon Galadiman Kano

Daga Sani Idris maiwaya   Mai Martaba Sarkin Kano na 16...

Babu wata baraka a hukumar NAHCON – Farfesa Abdullah Pakistan

Shugaban Hukumar kula da aikin hajji A ta Najeriya...