Daga Isa Ahmad Getso
Sanatan Kano ta kudu Sulaiman Abdulrahman Kawu Sumaila ya yabawa shugaban kasa Bola Tinubu bisa yadda ya amince da kasashe sama da Naira Biliyan 124 wajen karasa aikin titin Kano zuwa Maiduguri.
Ina mai farin cikin sanar da al’ummar mazabata ta kano ta Kudu da Kano, mutanen Najeriya baki daya, cewa bayan kudirin da na gabatar a kan Sashin farko na titin Kano – Maiduguri da na gabatar a ranar 7 ga Mayu, 2024, Majalisar Zartarwa ta Kasa, karkashin jagorancin Shugaban Kasa, ta dauki kwararan matakai. An soke kwangilar da aka bayar a baya kuma an sake ba da aikin hanyar ga kamfanin Triacter Construction”.
Kadaura24 ta rawaito Sanata Kawu Sumaila ya bayyana hakan ne a sashin shafinsa na Facebook da yammacin ranar talata.

Ya ce ” An bayar da sabuwar kwangilar ne wadda aka ba da ita akan kudi Naira Biliyan Dari da Ashirin da Hudu, Naira Miliyan Dari Hudu (₦124,400,000,000), kuma an baiwa kamfanin awa’adin shekaru uku domin ya kammala aikin.
“Wannan sashe na titin, wanda ya dade da zama tarkon mutuwa—wanda ke haifar da hadurruka akai-akai, da asarar rayuka, da cunkoson ababen hawa— yanzu zai samu kulawar gaggawa da ya kamata.
Yanzu-yanzu: Sarki Sanusi ya nada sabon Galadiman Kano
Ya ce wannan kundin ya tabbatar da aniyarsa ta kawo ababen more rayuwa ga al’ummarsa don inganta rayuwarsu.
Ya kara da cewa “Ina fatan in mika godiyata ga Majalisar Dattawan Najeriya, da abokan aikina da Ministan Ayyuka, da kuma Maigirma Shugaban Kasa bisa kokarinsu na ganin wannan aikin mai muhimmanci ya tabbata.