Wani Abun Fashewa Ya Tashi A Cikin Kasuwa A Jihar Yobe

Date:

Wani abun fashewa da ake zargin bam din da aka birne ne ya tarwatse a fitacciyar kasuwar dabbobin nan ta Buni Yadi dake karamar hukumar Gujba ta jihar Yobe.

Wani mazaunin garin Buni Yadin, Ali Hassan ya shaidawa tashar talabijin ta Channels ta wayar tarho cewar, al’amarin ya faru ne da misalin karfe 12 da rabi na ranar yau Juma’a, kuma ya raunata wata yarinya.

Talla
Talla

Shima kakakin shiya ta 2 na aikin wanzar da zaman lafiya na hadin gwiwa mai taken “Operation Hadin Kai”, Kyaftin Muhammad Shehu ya tabbatar da afkuwar lamarin, inda ya ce sojoji sun yi nasarar gano wani bam din da aka birne a kasuwar tare da tarwatsa shi.

Zanga-zanga: Abubuwan da Tinubu ya fadawa Malamai da Sarakuna a ganawarsa da su

Ya kara da cewa mutum guda da fashewar ta shafa, na samun kulawa a daya daga cikin asibitocin da ke garin Buni Yadi.

Ya kuma jaddada cewa al’amarin ba harin kunar bakin wake bane illa kawai bam ne da aka birne a kasa.

Talla

Garin Buni Yadi mai tazarar kilomita 54 tsakaninsa da Damaturu babban birnin jihar, na cikin karamar hukuma a jihar da ta fi fama da ayyukan ta’addanci, inda ta kasance karkashin mayakan Boko Haram tsawon shekaru 2.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...