Kungiyar kwallon kafa Barau FC ta dakatar mai horar da yan wasan ta Salisu Yusuf

Date:

Kungiyar kwallon kafa ta Barau FC ta dakatar da babban mai horar da yan wasan ta Salisu na tsahun wani lokaci nan take daga aikinsa.

Hakan na kunshe cikin wata sanarwa da kakakin kungiyar ta Barau FC Ahmad Hamisu Gwale ya sanyawa hannu, kuma mataimakinsa Ashiru Rabi’u Gidan Tudi ya aikowa Kadaura24.

Talla

Ya ce an dauki wannan matakin ne bayan taron da shugaban cin kungiyar ta gudanar sakamakon halin da take ciki a wannan kaka ta 2024-2025 na rashin samun nasarori a wasannin gida da waje.

Sanarawar taci gabata da cewa an yankin shawarar tabbatar da Rabi’u Tata, a matsayin wanda zai maye gurbin Salisu Yusif a matakin na rikon kwarya a dukkanin wasannin ta a nan gaba.

Sabon mai baiwa Gwamnan Kano shawara ya rasu kwana ɗaya da rantsar da shi

Kungiyar kwallon kafa ta Barau FC dai na fafatawa ne a gasar Firimiya ta Najeriya mai daraja ta biyu NNL, inda yanzu haka take a cikin rukuni na C da ya fito daga yankin Arewawaci Najeriya.

Hakazalika cikin wasanni hudun data buga yanzu haka na dauke da maki biyu ne a cikin rukuni, yayin da a ranar Asabar zata karbi bakwancin kungiyar kwallon kafa ta Sokkoto United a wasa mako na biyar duka a cikin rukunin na C.

Daga karshe mahunkutan kungiyar ta Barau FC sun yaba da irin kokarin da Salisu Yusuf yayi, a lokacin da ye rike da kungiyar a tsahun wasannin da ya fafata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Yusuf ya taya Dangambo murnar zama shugaban kungiyar mawallafa labarai ta internet na Kano

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Hajjin bana: Za mu yi duk abun da ya dace don kyautata walwalar alhazan Jihar Kebbi – Amirul Hajji

Daga Ibrahim Sidi Muhammad Jega.   Shugaban kwamitin aikin hajin bana...

Bayan dawo da Gwadabe Anti daba, Yansanda sun kama yan daba 33 a Kano

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar Yansanda ta Kasa reshen jihar...

Sabon Rikici ya Barke a Jam’iyyar NNPP ta Karamar Hukumar Dawakin Tofa

Rikici ya barke a cikin jam’iyyar NNPP ta karamar...