Musa Iliyasu Kwankwaso ya zama dan takarar Majalisar Kura Madobi da Garum mallam a APC

Date:

Daga Safyanu Dantala Jobawa

Tsohon kwamishinan raya karkara na jihar kano Dr Musa Iliyasu Kwankwaso ya lashen zaben fidda gwani na takarar dan majalisar tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Kura/Madobi/Garun mallam.

 

Yayin zaben Musa Kwankwaso ya lashe zaben ne da kuru’u 150, yayin Dan Majalisa Mai Wakiltar yankin Hon Kabiru Danhassan ya sami kuru’u 4, sai kuma Hajiya Hama Ali Aware Garun mallam ta sami 6.

Musa Iliyasu Kwankwaso dai tsohon Kwamishinan Ma’aikatar raya karkara ne a zamanin mulkin Malam Ibrahim Shekarau da Dr. Abdullahi Umar Ganduje.

 

Yanzu dai Hon. Musa Iliyasu Kwankwaso shi ne zai wakilci jam’iyyar APC a Babban zabe Mai zuwa na shekarar 2023, Inda ake ganin Zai iya yin nasara Saboda farin jinin da yake da shi a wurin al’ummar yankin Kura Madobi da Garum mallam.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Mamallakin jaridar Nigerian Tracker ya zama Ma’ajin kungiyar masu yada labarai a kafar yanar gizo ta Arewa

Kungiyar masu yada labarai a kafafen sadarwa na zamani...

Rusau: Ana zargin an harbi mutane 6 a unguwar Rimin zakara dake Kano

Daga Nazifi Dukawa   Mazauna Unguwar Rimin Zakara da ke Karamar...

Da dumi-dumi: Bayan dakatar da Sojaboy daga Kannywood, wata masarautar a sokoto ta tube rawaninsa

Masarautar Gidan Igwai ta dakatar da Usman Umar wanda...

Masu yada hotunan Akpabio a ofishin SDP suna yi ne don bata sunan Jam’iyyar – Hon. Ali Shattima

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban Jam'iyyar SDP na jihar Kano...