Masu yada hotunan Akpabio a ofishin SDP suna yi ne don bata sunan Jam’iyyar – Hon. Ali Shattima

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Shugaban Jam’iyyar SDP na jihar Kano Hon. Ali Shattima Tudun Murtala ya musanta labarin dake yawo a shafukan sada zumunta cewa shugabannin majalisar dattawan Nigeria sun Kai wata ziyara ofishin Jam’iyyar ta su.

” Yadda ku ka ga Wannan hotunan nima haka na gansu, amma abun da suke yadawa karya ce , domin tsohon hoto ne da aka dauke shi kusan sama da shekara guda data gabata”.

InShot 20250115 195118875
Talla

Hon. Ali Shattima ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa ta musamman da yayi da jaridar Kadaura24 ranar lahadi.

 

” An dauki hoton ne lokacin da Shugabannin majalisar Sanata Godswil Akpabio da Barau Jibrin suka ziyarci ofishin Jam’iyyar SDP kamar yadda suka ziyarci na jam’iyyun PDP da LP da NNPP domin neman goyon bayan sanatocin jam’iyyun kafin su zama Shugabannin majalisar”. Inji Hon. Ali Shattima

Babban Dalilin da ya sa na Shiga Siyasa – Sani Danja

Ya ce masu yada tsofaffin hotunan suna yin haka ne saboda sun ga yadda jam’iyyar SDP ta yunkuro domin ta karbi kasar nan.

Hon. Ali Shattima Tudun Murtala ya bukaci al’ummar Nigeria da su yi watsi da masu yada wadancan hotuna saboda suna yi ne kawai don bata Jam’iyyar SDP a wajen al’ummar Nigeria

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...

Tinubu ka fadawa yan Nigeria Inda ka tsaya har kwana 5 bayan taron BRICS – ADC

    Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC ta soki Shugaban...

Da dumi-dumi: Yadda akai Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami'an tsaro a Nigeria...