Mamallakin jaridar Nigerian Tracker ya zama Ma’ajin kungiyar masu yada labarai a kafar yanar gizo ta Arewa

Date:

Kungiyar masu yada labarai a kafafen sadarwa na zamani ta Arewancin Najeriya ta zabi Shugaban kafar sadarwa ta Nigerian Tracker Abbas Yushe’u Yusuf a matsayin Ma’ajin kudinta.

Kungiyar ta yi zaben ne a ranar Asabar lokacin zaben sabbin shugabanninta na yankin Arewa.

An shirya zaben ne a Kaduna karkashin jagorancin kwamatin da aka dorawa alhakin shirya zaben Kungiyar na Kasa.

InShot 20250115 195118875
Talla

Kwamared Musa Muhammad daga jihar Kaduna shine ya zama sabon shugaban Kungiyar ta masu tada labarai a kafar sadarwa ta zamani na kasa shiryar ta Arewa (Online Media).

Muhammad ya samu kuri’u 287 inda ya kayar da abokin takararsa, kwamared Lynn Adda, tsohon shugaban Kungiyar yan jarida NUJ na jihar Taraba, wanda ya samu kuri’u 138.

Kwamared Femi Adi daga jihar Kogi shine ya zama babban sakataren Kungiyar da kuri’u 210 Inda ya kayar da kwamared Rayyan Al-Hassan, wanda ya samu kuri’u 207.

Rusau: Ana zargin an harbi mutane 6 a unguwar Rimin zakara dake Kano

Sauran wadanda suka fito babu hamayya sun hada da kwamared Zaharaddeen Ishaq Zailani da ya zama Sakataren kudi na kasa da kwamared brahim Suleman Mataimakinsa Mataimakin Sakataren kuɗi.

Sai kuma kwamared Abbas Yusha’u Yusuf daga Kano da ya zama Ma’ajin kudi na kasa.

A jawabinsa na karabar ragamar Shugabancin Kungiyar na Arewa Kwamared Musa Mohammed ya bukaci ‘ya’yan kungiyar da ke jihohin Arewa 19 da su yi amfani da kafafen sada zumunta wajen yakar labaran karya da inganta shugabanci na gari.

Acewarsa,kafar sada zumuntar na yanar gizo na iya zama abin dogaro ne kawai don yada labarai lokacin da kwararrun ‘yan jarida suka karbe ragamar aiki tare da amfani dashi ta hanyar kwarewa. na zamani ta Arewancin Najeriya ta zabi Shugaban kafar sadarwa ta Nigerian Tracker Abbas Yushe’u Yusuf a matsayin Ma’ajin kudinta.

Da dumi-dumi: Bayan dakatar da Sojaboy daga Kannywood, wata masarautar a sokoto ta tube rawaninsa

Kungiyar ta yi zaben ne a ranar Asabar lokacin zaben sabbin shugabanninta na yankin Arewa.

An shirya zaben ne a Kaduna karkashin jagorancin kwamatin da aka dorawa alhakin shirya zaben Kungiyar na Kasa.

Kwamared Musa Muhammad daga jihar Kaduna shine ya zama sabon shugaban Kungiyar ta masu tada labarai a kafar sadarwa ta zamani na kasa shiryar ta Arewa (Online Media).

Muhammad ya samu kuri’u 287 inda ya kayar da abokin takararsa, kwamared Lynn Adda, tsohon shugaban Kungiyar yan jarida NUJ na jihar Taraba, wanda ya samu kuri’u 138.

Kwamared Femi Adi daga jihar Kogi shine ya zama babban sakataren Kungiyar da kuri’u 210 Inda ya kayar da kwamared Rayyan Al-Hassan, wanda ya samu kuri’u 207.

Sauran wadanda suka fito babu hamayya sun hada da kwamared Zaharaddeen Ishaq Zailani da ya zama Sakataren kudi na kasa da kwamared brahim Suleman Mataimakinsa Mataimakin Sakataren kuɗi.

Sai kuma kwamared Abbas Yusha’u Yusuf daga Kano da ya zama Ma’ajin kudi na kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...