Hayar Gidaje: Dole Masu Unguwanni ku tashi tsaye don kyautata tsaro-Aranposu

Date:

Daga Aisha Ahmad Dorayi

Shugaban Karamar Hukumar Nasarawa Alh. Auwal Lawan Shu’aibu ya bayyana cewa ya Zama wajibi kowanne Mai unguwa a Karamar Hukumar idan an sayi fili ko Gida a yankinsa ya sanar da Dagacin Wannan yanki domin kyautata al’amuran tsaro a yankin.

Shugaban Karamar Hukumar ya bayyana hakan ne Yayin wata ganawa da sukai da Masu Unguwannin yankin domin cigaban tsaron Karamar Hukumar.

Auwal Lawan yace Saboda yadda ake samun Shigowar Baki jihar nan akwai bukatar a Dauki irin wadannan Matakai domin sanin da suwa ake mu’amala.

Yace ya Zama wajibi Mai unguwa ya sanar da Dagaci irin Cinikin da aka Yi a yankinsa Koda kuwa Cinikin karamine

“mun Dauki Wannan Matakinne don Inganta Tsaro ba don mu musgunawa kowa ba, Kuma ai idan ka Sami abun da zaka samu ta tsaftacetacciyar hanya Yama fi kaci kudinka ba tare da Rashin hankali ko Kuma kasa Rayuwar al’umma Cikin hadari”. Aranposu

Shugaban Karamar Hukumar ta Nasarawa ya Kuma ce Suma dillalai Masu bada hayar Gidaje akwai tsari da akai domin kyautata sana’arsu.

“Mun Samar da form Wanda za’a Rika baiwa duk Wanda yazo domin kama haya , Wanda a Cikinsa Mai unguwa da dagaci zasu da hannun, Sannan Kuma shi ma Mai kama hayar sai ya Kawo Wanda Zai tsaya Masa”. Inji Aranposu

Alhaji Auwal Lawan Shu’aibu ya bada tabbacin Karamar Hukumar zata Hukunta duk Wanda aka samu da Karya Dokokin da aka gidaya.

Suma Masu Unguwannin sun bada tabbacin bada hadin Kan da ake fada domin kyautata al’amuran tsaro a Karamar Hukumar ta Nasarawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar kafafen yada labaran yanar gizo ta bukaci gwamnatin Kano ta gyara hanyoyin dake karkara

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Kungiyar kafafen yada labarai na yanar...

Gwamnatin Kano za ta sake gina Masallacin da aka kona a Gezawa

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin gwamna...

Hukumar shari’a ta Kano ta ladaftar da wasu ma’aikatan kotu

Daga Usman Hamza   Hukumar Kula da Harkokin shari'a ta Jihar...

2027: Malam Shekarau ya bayyana matsayar kungiyarsu kan hadakar yan hamayya a Nigeria

Ƙungiyar siyasa ta Northern Democrats, ƙarƙashin jagorancin Malam Ibrahim...