Kotu ta Umarci gwamnatin Kano ta biya diyyar rushe ginin Asibitin Tiamin

Date:

 

 

Babbar Kotun Jihar Kano ta yanke hukuncin cewa matakin da gwamnatin jihar ta dauka na kwace fili da rushe ginin asibitin zamani da kamfanin Tiamin Multi Services Global Limited ke ginawa a unguwar Gyadi-Gyadi, karamar hukumar Tarauni, ya sabawa doka.

Kotun ta umarci gwamnatin jihar da ta biya kamfanin diyya da ta kai Naira biliyan 2.635 sakamakon wannan take hakki.

IMG 20250415 WA0003
Talla

A cewar bayanan kotu, gwamnatin da ta gabata a karkashin tsohon Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ce ta kwace filin tare da rushe gine-ginen da aka kusa kammalawa a wancan lokaci.

Kamfanin Tiamin ya shigar da kara tun a watan Oktoba na shekarar 2019, yana neman diyya kan abin da ya bayyana a matsayin take hakkin mallaka da rushe asibitinsa ba tare da bin ka’idojin doka ba.

A hukuncin da Mai shari’a Ibrahim Karaye ya yanke a ranar Laraba, kotun ta bayyana cewa kwace filin da gwamnatin Kano ta yi a ranar 3 ga Satumba, 2021, ta hanyar wasika daga Hukumar Kula da Filaye ta Jihar Kano, ya saba da kundin tsarin mulki da kuma dokar mallakar fili ta ƙasa (Land Use Act).

InShot 20250309 102403344

Mai shari’a Karaye ya jaddada cewa gwamnatin jihar ta dauki matakin ne ba tare da bai wa kamfanin damar kare kansa ba, lamarin da ya sa kwace filin da kuma rushe ginin suka zama babu inganci a idon doka.

Kotun ta kuma soki gwamnatin jihar bisa matakin rushe ginin yayin da karar ke gaban kotu, tana mai bayyana hakan a matsayin saba wa doka da kuma abin kyama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...