Gwamnatin Kano za ta sake gina Masallacin da aka kona a Gezawa

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin gwamna Abba Kabir Yusuf ta ware kudi domin sake gina masallacin da wani mutum ya bankawa wasu masallata wuta yayin da suke sallar asuba a karamar hukumar Gezawa.

A wata sanarwa da jami’in yada labaran yankin Jamilu Mustapha Yakasai ya aikowa Kadaura24, ya ce Shugaban karamar hukumar Gezawa, Alhaji Mukaddas Bala Jogana, ya bayyana cewa, baya ga sake gina masallacin, gwamnatin za ta kuma gina ajujuwa, da bandakuna, da rijiyar burtsatde a harabar masallacin.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Mukaddas ya kara da cewa gwamnatin jihar ta kammala aikin titin kilomita 5 na karamar hukumar.

Hukumar shari’a ta Kano ta ladaftar da wasu ma’aikatan kotu

Ya yi kira ga ma’aikatar ayyuka da ta fara aikin titin Dan Madanho zuwa Kwasangwami zuwa Zango, wadda ya ce hanya ce mai muhimmanci da al’umma da dama ke amfani da ita.

Alhaji Mukaddas Bala ya nuna matukar godiya ga Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa kokarinsa na daukaka martabar jihar Kano. Ya kuma yi kira ga al’ummar Kano da su ci gaba da marawa gwamnatin gwamna Abba Kabir Yusuf baya.

InShot 20250309 102403344

Shugaban karamar hukumar Gezawan ya yi alkawarin za’a ci gaba da gudanar da ayyukan raya kasa don amfanin al’ummar yankin, musamman a fannonin kiwon lafiya, ilimi, da sauransu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...