Ban ce filin makarantar Bechi nawa ba ne, Kuma zan taimaka wajen gini Makarantar – Alh. Sagir Jaen

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

Biyo bayan koken da al’ummar garin Bechi dake karamar hukumar Kumbotso a jihar Kano, da su ka yi ga gwamnan Kano Alh Abba Kabir Yusif na siyar da filin wata makarantar sakandiren mata dake yankin.

Yanzu haka Mamallakin filin da ake takardama akan sa a garin Bechi, Alhaji Sagir Isyaku Ja’en, ya bayyana asali yadda ya Mallaki filin a hannun wani Mutum Mai suna Farfesa Ibrahin Shehu, da shine ya siyar Masa da wajen, tun shekarar 2015, Kuma yana da cikakun takardun shedar mallaka daga kowace Hukumar da doka ta tanada.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Alhaji Sagir Ja’en, ya ce ya yi mamakin yadda ya ji mutane na korafi kan wannan fili, duk da cewa batun ya na gaban hukumomi don tantancewa, kuma ya kai dukanin wasu hujjoji domin tantance gaskiyar lamarin.

Wasu mutane na kokarin sayar da wata makaranta a Kano, al’ummar yankin sun nemi daukin gwamna Abba

Ya kara da cewa tun asali wannan gini da ake takardama akan sa na shedar ginin Makaranta, baya cikin gurin daya mallaka, kuma bai ce nasa bane, shi ma zai iya gina Makarantar domin al’umma su amfana” inji Alh Sagir.

Haka zalika Alh Sagir Ja”en ya yi kira ga al’ummar yankin su kwantar da hankalin su, Babu abin da zai taba ginin makarantar domin ba mallakinsa bane, kuma zai basu gudunmawar data kamata wajen gina Makarantar, Dalibai su yi karatu sosai.

InShot 20250309 102403344

“A karshe Alhaji Sagir Isyaku ya godewa al’ummar garin Bechi yadda suke kokarin kawo zaman lafiya,kwanciyar hankali, yana mai cewa insha Allahu zai tabbatar da kowa ya samu Nasara domin cigaban garin Bechi da kewaye.” Sagir Ja’en

Alhaji Sagir Ja’en ya kuma turowa kadaura24 wasu daga cikin shidar mallakar filin dake kusa da makarantar da ake takaddama akansa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...