Ranar Damokaradiyya: Ganduje yace Zai yi Magani Yan takarar da Suka sa aka Daga Fastar sa

Date:

Daga Abubakar Sa’eed

Gwamnan jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya gargadi Yan Siyasa da Yan takara da su guji sa a Daga Hotunan su a taron Ranar Damokaradiyya ta bana da za’a gudanar Ranar Asabar.

Ganduje ya bayyana hakan ne Yayin Bikin baiwa Matasa da Dalibai Motoci domin bunkasa harkokin su.

Ganduje yace ba zai lamunci Yan Siyasa su Rika sawa ana Daga Hotunan su a Yayin taron Ranar Damokaradiyya ba Saboda akwai Manyan Baki da zasu Shigo jihar nan.

“Duk Dan takarar da ya baiwa Matasa Kayan maye ko Makami suka shiga dasu wajen taron mu to da kaina Zan sa a Kama yaron, Sannan Kuma Zan yi Maganin Wanda ya basu”. Inji Ganduje

Yace Shugaban jam’iyyar APC na Kasa da sauran Shugabanin jam’iyyar Za su halarci wajen taron na Ranar Damokaradiyya ta bana.

Gwamna Ganduje yace bayan Sunan Shugaban Kasa Muhd Buhari da Sunan Shugaban jam’iyyar APC na Kasa dana Gwamna Kano bama so muji an kirawo Sunan Wani Dantakara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...

Sarkin Yaƙin Garko, ya ɗauki nauyin dubawa da raba magunguna kyauta ga marasa lafiyar 1400 a Garko

  Sarkin Yaƙin Garko, mai kishin al'umma, kuma ɗan jam'iyyar...

NAHCON ta yi jigilar Maniyatan Nigeria Sama da 24,000 zuwa Saudiyya a kwanaki 10

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar Kula da aikin hajji ta...