Muaz magaji ya kurmance, yayin da kotu ta bada Umarnin kai shi Asibiti

Date:

Daga Mubarak Ibrahim
Wata kotun majistare da ke Kano ta saurari karar tsohon kwamishinan ayyuka da samar da ababen more rayuwa na Kano, Muaz Magaji, wanda ya “rasa jinsa” bayan wani hatsarin da yayi Sakamakon bin da ‘yan sanda suka yi Masa a Abuja a ranar Alhamis.
Kadaura24 ta rawaito an kama Muaz Magaji ne bayan ya Kasa sarrafa motarsa ​​tare da afwa fitilar wutar titi.
 Da ya bayyana a gaban Alkalin Aminu Gabari a ranar Juma’a, Lauyan Magaji, Garzali Ahmad, ya ce wanda yake karewa ya rasa jinsa na dan wani lokaci sakamakon raunin da ya samu bayan hatsarin da yayi.
 Barr. Ahmad ya kara da cewa wanda ake tuhumar ba zai iya sauraron tuhumar da ake yi masa ba kuma har ya amsa tuhumar.
 Don haka ya roki kotu da ta bayar da belin wanda yake karewa domin neman lafiyarsa.
 Da yake yanke hukunci kan lamarin, Mai Shari’a Aminu Gabari ya ba da umarnin a kai Muaz Magaji asibitin ‘yan sanda kuma ya ci gaba da zama a hannun ‘yan sandan.
 Ya dage sauraron karar zuwa ranar Litinin 31 ga watan Janairu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...