Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Date:

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya Lokacin Zaɓen Shugaban Ƙasa Da Na Gwamnoni Zuwa Nuwamba, 2026

An gabatar da Kudirin Gyaran Dokar Zaɓe ta 2025 (Electoral Act Amendment Bill 2025) a yayin zaman sauraron ra’ayoyin jama’a da aka gudanar a Abuja a ranar Litinin, wanda Kwamitocin Majalisar Dattawa da na Majalisar Wakilai kan Harkokin Zaɓe suka shirya tare.

A cikin kudirin, majalisar ta ba da shawarar a gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na gwamnonin jihohi a watan Nuwamba, 2026, wato watanni shida kafin lokacin da ake gudanar da irin wannan zaɓe a da.

Kudirin ya tanadi cewa, “Zaɓen ofishin shugaban ƙasa da na gwamnan jiha dole ne a gudanar da shi ba fiye da kwanaki 185 kafin karewar wa’adin mai rike da mukamin a yanzu.”

Wannan sabon tsarin zai sa zaɓukan gaba na ƙasa da jihohi su gudana a Nuwamba, shekarar 2026.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...