Kotu ta ba da umarnin kamo jarumi Sadiq Sani Sadiq

Date:

Daga Jamilu Bala

Kotun shari’ar Musulunci da ke Hotoro Masallacin Juma’a ta bayar da umarnin da a kamo mata Jarumin wasan Hausan Sadiq Sani Sadiq.

Wani mai shirya fina-finai Aliyu Muhammad Hannas, ne ya shigar dakarar a gaban kotun kan cewar ya baiwa jarumin kudi domin yayi masa aikin film, amma yaki zuwa don yin aikin, Inda yace hakan ya ja masa asara mai yawa.

Jarumi Sadiq Sani Sadiq

Alkalin Kotun Maishari’a Sagiru Adamu, yace Sadiq ya bijirewa Umarnin Kotu duk da sammacin da aka bashi, tare da like masa sammacin a jikinm gidansa amma yaki halartar zaman kotun.

 

Zuwa yanzu dai kotun ta baiwa Dan sandan Kotun umarnin kamoshi, duk inda yake zuwa gaban kotun.

Express Radio ta rawaito Kotun tace da zarar an kamo Jarumin wasan hausan Sadiq Sani Sadiq, za a cigaba da zaman sauraren shari’ar.

2 COMMENTS

  1. Its like you learn my thoughts! You appear to understand a lot about
    this, such as you wrote the guide in it or something.

    I think that you just could do with some p.c. to pressure the
    message home a little bit, but instead of that, that is great blog.
    An excellent read. I’ll definitely be back.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu ta ɗaure wani ɗan Tiktok mai wanka a tsakiyar titunan Kano

    Wata kotu a jihar Kano da ke arewacin Najeriya...

Damuna: Mun shirya inganta wuraren tsayarwar motocinmu – Kungiyoyin Direbobin na Kano

Kungiyar matuka motocin kurkura ta jihar Kano da Kungiyar...

Rasuwar Aminu Ɗantata babban rashi ne ba ga Nigeria kadai ba – Mustapha Bakwana

Daga Zakaria Adam Jigirya   Tsohon Mai baiwa gwamnan Kano shawarawa...

Gwamnatin Kano ta yabawa Tinubu saboda gyarawa da bude NCC DIGITAL PARK

Daga Rahama Umar Kwaru   Gwamnatin jihar Kano ta yabawa Gwamnatin...