Farfesa Gwarzo Ya Samu Lambar Karramawa A Faransa, Wakiliyar UNESCO Ta Halarta

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Jami’ar Cité Universitaire de Paris, daya daga cikin fitattun jami’o’i a Faransa da ake darajawa, wacce ke matsayi na 12 a fadin Turai, ta karrama Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo, Shugaban Ƙungiyar Jami’o’i Masu Zaman Kansu na Afirka (AAPU), da Lambar Girmamawa mai daraja saboda gudunmawar sa wajen bunkasa ilimi a Afirka da ma duniya baki ɗaya.

An mika lambar yabon ne a ranar Juma’a, 13 ga watan Yuni, 2025, ta hannun Shugaban Jami’ar, Sanata Jean Mac Sauve, inda aka gudanar da bikin a matsayin wani bangare na shagulgulan cika shekaru 100 da kafuwar jami’ar, da kuma wani taron kasa da kasa kan bunkasa ilimi da bincike a Afirka.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Taron ya samu halartar manyan masana daga jami’o’i daban-daban na duniya. A jawabinsa, Sanata Jean Mac Sauve ya bayyana jin daɗinsa da irin rawar da Farfesa Gwarzo ke takawa wajen wakiltar Faransa cikin kima a Afirka, kasancewar sa ɗan tsohuwar makarantar ta Faransa.

Ya yabawa Farfesa Gwarzo kan yadda yake zuba hannun jari a bangaren ilimi tare da sadaukarwar da yake yi wajen bunkasa manyan makarantu a Nijeriya da Afirka baki daya, yana mai cewa hakan abin yabo ne matuƙa.

Wakiliyar Dindindin ta Nijeriya a UNESCO, Jakadiya Dr. Hajo Sani, ita ce ta wakilci Nijeriya a wajen bikin, inda ta yabawa jami’ar bisa zaɓar Farfesa Gwarzo a matsayin wanda ya cancanci wannan girmamawa. Ta ce wannan yabo babbar shaida ce kan jajircewar Farfesan wajen ci gaban ilimi da tasirinsa ga al’ummar ilimi gaba ɗaya.

Kwacen waya: Ya kamata gwamnatin Kano da hukumomin tsaro su tashi tsaye – Auwal Danlarabawa

Jakadiya Hajo Sani ta kara da cewa Farfesa Gwarzo ya ba da gudunmawa sosan gaske kuma mai tsoka ta hanyar kafa jami’o’i guda uku a Nijeriya, inda ta bayyana cewa har ‘ya’yanta biyu suna daga cikin waɗanda ke cin moriyar wannan gagarumin ci gaba.

A nasa bangaren, Farfesa Gwarzo ya nuna godiya ga jami’ar ta Faransa bisa wannan lambar girmamawa da aka ba shi, yana mai nanata kudurinsa na ci gaba da inganta harkar ilimi ba kawai a Afirka ba, har ma a duniya baki ɗaya.

Ya kuma yi kira ga dukkan ‘yan Afirka da ke karatu a ƙasashen waje da su dawo gida bayan kammala karatu, domin ba da gudunmawa wajen gina nahiyar Afirka da har yanzu ke da buƙatar ci gaba.

InShot 20250309 102403344

A karshe, Farfesa Gwarzo ya ce wannan lambar yabo za ta ƙara masa ƙwarin gwiwa wajen ci gaba da jagorantar gamayyar jami’o’in MAAUN zuwa ga samar da ingantaccen ilimi mai tasiri ga ci gaban rayuwar al’umma.

Lambar Girmamawar ta zama wata kwakkwarar shaida ta irin tasiri da sadaukarwar Farfesa Gwarzo wajen haɓaka ilimi a matakin duniya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...