Mun gano dalilan yan adawa na daukar nauyin fadan daba a birnin Kano – Gwamnatin kano

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Gwamnatin jihar Kano ta nuna takaicinta akan yawaitar fadace fadacen daba a birnin Kano da kewaye dake sanadiyar rasa rayukan jama’a.

Sai dai gwamnatin Kano ta alakanta fadan dabar da siyasa da ta ke zargin wasu yan hamayya da rura wutar rikicin dabar domin bata sunan gwamnatin.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Kwamishinan kananan hukumomi na Kano, Hon Muhammad Tajuddeen othman ne ya bayyana hakan a lokacin da ake tambayarsa kokarin da gwamnatin kano ke yi don magance fadan Daba ta cikin wani shiri Mai suna ”Gwamnati da jama’a” wanda aka gudanar a tashar Rahma Radio da ke Kano.

Kwamishinan ya yi zargin wasu daga cikin yan siyasa da daukar nauyin fadan Dabar a birnin Kano domin cimma wata manufa ta su ta siyasa.

Kwacen waya: Ya kamata gwamnatin Kano da hukumomin tsaro su tashi tsaye – Auwal Danlarabawa

Hon. Tajuddeen othman ya tabbatarwa da jama’ar Kano cewa gwamnati na iya kokarin ta wajen magance matsalar ta hanyar daukar matasa aikinyi da sanyasu a makarantu.

Kwamishinan ya kuma shaida cewa kwamatin da gwamnatin kano ta kafa na magance fadan Daba karkashin jagorancin kwamishinan ma’aikatar kimiya da fasaha Dr Yusuf Ibrahim Kofar Mata na aiki dare da rana domin samar da tsaro a Kano.

InShot 20250309 102403344

Idan za’a iya tunawa daga ranar laraba zuwa safiyar Juma’a da Asabar fadacen fadacen dabar da kwacen waya yayi salwantar rayuwakan matasa biyu a birnin Kano ,Inda kuma fadan dabar ya hana jama’a sakat a cikin birnin.

Kwamishinan ya shaida cewa tabbatar da kare rayukan jama’a da dukiyoyin mutanan Kano na daga cikin kudurin gwamna Abba Kabir Yusuf tun kafin hawansa mulkin Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abubakar Bichi ya bada gudumawar motocin bas 13 ga jami’o’in Kano da taraktoci 11 ga yan mazabarsa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Dan Majalisar tarayya mai wakiltar karamar...

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...