Jan fentin da aka sanya a Rimin Zakara ba na rusau ba ne, na kawo cigaban gwamnna ne – Nazifi Tijjani

Date:

Daga Nazifi Dukawa

 

Shugaban Kungiyar masu siyar da filaye, gidaje da kangwaye kuma mai kamfanin Annatija Properties Alhaji Naziru Tijjani Idiris ya karyata labarin rusau a garin rimin zakara da wani yayi zargi.

Alh Naziru Tijjani Annatija ya ce sanya Jan fenti alkhairi ne ya zo garin gwamnnatin jihar kano ce ta zo da karin cigaba a garin don cigaban da farantawa al’ummar yankin.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Ya ce waccen maganar ta tunani za a sake yin rusau a gari babu kamshin gaskiya a cikinta .

“Idan za a yi rusau ana rubuta alamar rushewa , Amma wanan kuma alama ce ta kidaya gidajen da kangwaye ce domin cigaban da tallafawa mazauna yankin”. Inji Naziru Tijjani

Al’ummar Rimin Zakara sun musanta zargin sake yin Rusau a garin, sun kori wanda ya yi zargin

Alhaji Naziru Tijjani Annatija ya ce idan mutane za su iya tunawa a baya gwamnan ya yi alkawarin kawo wutar lantarki yankin da asibiti da makaranta har ma da masallacin Juma’a.

InShot 20250309 102403344

“A halin yanzu kullum ma’aikatan gwamnnatin su na zuwa yankin don cigban da kawo ayyukan alkhairi a yankin don haka masu gidaje da filaye da kangwaye su kwantar da hankalinsu babu abun da zai faru.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...

Tinubu ka fadawa yan Nigeria Inda ka tsaya har kwana 5 bayan taron BRICS – ADC

    Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC ta soki Shugaban...

Da dumi-dumi: Yadda akai Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami'an tsaro a Nigeria...