Kwacen waya: Ya kamata gwamnatin Kano da hukumomin tsaro su tashi tsaye – Auwal Danlarabawa

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Kungiyar Grassroot Care and Aid Foundation ta nemi Gwamnatin Jihar Kano da hukumomin tsaro su gaggauta ɗaukar mataki kan yawaitar matsalar kwacen waya da fadace-fadacen daba da ke jefa rayukan al’umma cikin haɗari.

Kadaura24 ta rawaito wannan na cikin wata wasika da shugaban ƙungiyar, Amb. Auwalu Muhammad Danlarabawa, ya aike wa Kwamishinan Harkokin Tsaro da sauran hukumomin tsaro na jihar, a ranar Asabar, 14 ga Yuni, 2025.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Kungiyar ta bayyana damuwa kan yadda matasa da mata da sauran marasa ƙarfi ke fuskantar barazana daga masu aikata laifuka, musamman a yankunan da aka fi samun fadace-fadacen daba da kwacen waya.

Dawo da Gwadabe ya Jagoranci Anti Daba Hanya ce ta Magance Fadan Daba a Kano

Ta bukaci a ƙara yawan sintiri da sa ido a wuraren da abin ya fi kamari, da kuma ƙarfafa dabarun tattara bayanan sirri tare da haɗin gwiwa da shugabannin al’umma da ƙungiyoyin matasa domin dawo da zaman lafiya.

InShot 20250309 102403344

Kungiyar ta kuma yaba da kokarin da hukumomin tsaro ke yi, tare da ƙarfafa gwiwarsu wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dr. Kabiru Getso Ya Mika Ta’aziyya Ga Iyalan Buhari

Daga Rahama Umar Gwaru   Tsohon kwamishinan ma'aikatun lafiya da muhalli...

Gwamnatin tarayya ta ayyana Ranar hutu saboda rasuwar Buhari

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta ayyana Talata, 15 ga watan...

Injiniya Iliyasu Usman Salihu ya zama Jakadan zaman Lafiya na Africa

    Injiniya Ilyasu Uasman Salihu, Manajan Darakta na Sadex Engineering...

Halin da ake ciki game da shirye-shiryen jana’izar Buhari

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda, ya bayayna cewa sai...