Kwamishinan Sufuri Na Kano Ya Janye Daga Karbar Belin Wanda Ake Zargi Safarar Miyagun Kwayoyi

Date:

Kwamishinan Sufuri na jihar Kano, Alhaji Ibrahim Namadi, ya janye matsayin da ya dauka na tsayawa beli ga wani da ake zargi da safarar miyagun kwayoyi a gaban kotu.

Sanarwar hakan na kunshe ne a wata takarda da mai taimaka masa na musamman kan harkokin yada labarai, Abdullatif Auta, ya fitar a ranar Juma’a.

InShot 20250309 102512486
Talla

A cewar sanarwar, Kwamishina Namadi ya rubuta wa kotu wasika ya na bayyana aniyarsa ta janye belin da ya tsaya wa Sulaiman Aminu Danwawu, wanda Hukumar NDLEA ke tuhuma da laifin safarar miyagun kwayoyi.

Dalilina na karbar belin Danwawu – Kwamishina Namadi

Kwamishinan ya ce ya dauki matakin janye belin ne saboda dalilai na kashin kai da kuma bukatar kare mutuncinsa da martabar ofishin da yake rike da shi.

Ya ce lokacin da ya tsaya wa Danwawu beli, ya yi hakan ne saboda alakar jini da ke tsakaninsu da kuma jin kai, amma ba saboda yana goyon bayan ayyukan da ake tuhumarsa da shi ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...