NiMet ta bayyana jihohin da za a sami tsawa da ruwan sama na kwanaki 3 a Nigeria

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

Hukumar hasashen yanayi ta Najeriya ta yi hasashen za a iya samun tsawa da ruwan sama a sassan Najeriya daban-daban daga ranar Lahadi 8 ga watan Yuni zuwa Talata 11 ga watan Yunin 2025.

Hukumar hasashen yanayin ta bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Asabar a Abuja.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Inda ta ce za a iya samun wannan yanayin a a sassa da dama na kasar, da suka hada da jihohin Arewa maso yamma, Arewa ta Tsakiya, da Kudancin kasar.

A cewar NiMet, ana sa ran ranar Lahadi za a fara da ganin gajimare a wurare da dama, amma zuwa yammacin ranar yanayi zai canza .

Sarki Sanusi ya hori musulmi su hada kai don cigaban addinin musulunci

Hukumar ta bayyana cewa “da rana ko yamma, ana iya samun tsawa tare da ruwan sama a sassan Taraba, Adamawa, Katsina, Kano, Zamfara, Kaduna, Jigawa, Borno, Gombe, da Bauchi.”

InShot 20250309 102403344

“A shiyyar Arewa ta Tsakiya, da safe ana sa ran za a sami gajimare a yankin.

“Washegari kuma ana hasashen tsawa da ruwan sama a wasu sassan babban birnin tarayya, Neja, Nasarawa, Kwara, Kogi, Benue da Plateau.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...