Sarki Sanusi ya hori musulmi su hada kai don cigaban addinin musulunci

Date:

 

 

Sarkin Kano na 16 Malam Muhammadu Sunusi na biyu, ya hori al’ummar Musulmi da su hada kawunansu don ci gaban addinin Islama.

Sarkin ya bayyana hakan ne yayin da ya gabatar da hudubar sallar Idi a babban masallacin Idi da ke Ƙofar Mata a Kano.

IMG 20250415 WA0003
Talla

“Masu hali ku ƙara himma wajen taimakon masu ƙaramin ƙarfi dake cikin al’umma musaman a wannan lokaci na sallar Idin Layya, don neman yardar Allah maɗaukakin Sarki, in ji Sarkin”.

InShot 20250309 102403344

Sarki Sanusi na biyu, ya kuma miƙa saƙon barka da Sallah, ga al’ummar Musulmi, inda ya buƙaci jama’a da su yi amfani da wannan dama wajen sanar da soke haye hayen Sallah, da aka saba gudanarwa bisa ga sha’anin kalubalen tsaro.

Daganan Sarkin ya kuma yi kira ga iyaye da su ƙara ƙaimi wajen sanya idanu ga tarbiyar ƴaƴansu, don kare su daga shiga gurɓatattun halaye na Daba da ƙwacen Waya da sauran munanan ayyuka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...