Soke Hawan Sallah: Dole Gwamnatin tarayya ta biya mu diyya – Gwamnatin Kano

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Gwamnatin jihar Kano ta bukaci gwamnatin tarayya ta biya ta diyya bayan da aka soke Hawan Sallah na tsawon shekaru biyu a jere.

Kwamishinan kananan hukumomi da masarautu na jihar, Alhaji Tajo Uthman ne ya yi wannan kiran a ranar Lahadi yayin da Sarkin Kano na 16, Alhaji Muhammadu Sanusi II ya kai wa Gwamna Abba Kabir Yusuf a gidan gwamnati.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Uthman ya ce jihar Kano ta tafka asara mai tarin yawa sakamakon soke hawan na al’ada wanda ake gudanarwa shekara-shekara wanda ya ke jawo hankalin masu yawon bude ido na cikin gida da waje.

“UNESCO ta amince da Hawan Sallar a matsayin bikin al’ada na gargajiya, wanda ake yi a lokacin bukukuwan sallah, Kano na samun makudan kudaden shiga daga kasashen waje saboda masu zuwa su kalli hawan daga ciki da wajen kasar nan,” in ji shi.

NiMet ta bayyana jihohin da za a sami tsawa da ruwan sama na kwanaki 3 a Nigeria

Kwamishinan Ya yi nuni da cewa, tasirin soke Hawan ya shafi tattalin arzikin kano wanda zai yi tasiri a kasafin kudin shekara mai zuwa na jihar.

Ya kuma jaddada cewa dole ne gwamnatin tarayya ta dauki alhakin Wannan asarar da ta jawowa jihar kano sakamakon soke Hawan don dale ne biya jihar diyya .

InShot 20250309 102403344

“Lokaci ya yi da za mu nemi a biya mu diyyar asarar da aka jawo mana,” in ji kwamishinan.

Uthman ya kuma yi kira da a gaggauta dawo da bukukuwan Hawan sallah a jihar Kano, yana mai bayyana sokewar a matsayin abin takaici.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Halin da ake ciki game da shirye-shiryen jana’izar Buhari

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda, ya bayayna cewa sai...

Rasuwar Buhari: Majalisar Nigeria ta dakatar da duk aiyukanta

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Majalisar dokokin Nigeria ta dage zamanta...

Gwamnati ta baiwa ma’aikata hutu saboda rasuwar Muhammad Buhari

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Katsina karkashin gwamna Umar...

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...