Gwamna Yusuf ya taya Dangambo murnar zama shugaban kungiyar mawallafa labarai ta internet na Kano

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya taya Abubakar Abdulkadir Dangambo murnar zama shugaban sabuwar kungiyar mawallafa labarai a yanar gizo ta jihar Kano dake karkashin kungiyar yan jaridu ta kasa (NUJ) .

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa Kadaura24 a ranar Litinin.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Gwamna Yusuf ya bayyana zabar Dangambo a matsayin wani mataki na cigaba a fagen yada labarai na zamani.

Ya kuma yabawa shugabannin kungiyar NUJ Kano a karkashin jagorancin Kwamared Sulieman Dederi bisa nasarar kafa sabuwar kungiyar ta mawallafa labarai a yanar gizo, wanda a cewarsa hakan zai kara kaimi ga kokarin da kafafen yada labarai na gargajiya suke yi wajen inganta gaskiya da gaskiya da rikon amana.

Hukumar Shari’a ta Kano ta Gargadi Alkalai 2, ta kuma dakatar da Magatakarda 2

Gwamnan ya bayyana cewa ya na da kwarin guiwar cewa a karkashin jagorancin Dangambo, kungiyar za ta sami gagarumin ci gaba a jihar Kano da ma sauran kasashen duniya.

InShot 20250309 102403344

Ya ba da tabbacin gwamnatinsa za ta baiwa kungiyar goyon bayan da hadin kan da ake bukata domin inganta aiyukan ya’yan kungiyar.

Gwamna Yusuf ya yi wa Kwamared Dangambo da sauran Shugabannin fatan samun nasara da kuma tasiri, inda ya bukace su da su yi aiki tukuru wajen bunkasa kungiyar da inganta aikin jarida.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Babbar Sallah: Gwamnatin Kano ta sanar da ranar rufe makarantu a jihar

Daga Rahama Umar Kwaru   Gwamnatin Jihar Kano ta bayar da...

Ban San Taulaci ba Sai da na Zama Sarkin Kano – Sarki Sanusi II

Daga Isa Ahmad Getso Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi...

Iftila:I: Gwamnatin Kano ta Aiyana Ranar Litinin a Matsayin Ranar Hutu

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar Litinin...

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...