Gwamna Yusuf ya taya Dangambo murnar zama shugaban kungiyar mawallafa labarai ta internet na Kano

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya taya Abubakar Abdulkadir Dangambo murnar zama shugaban sabuwar kungiyar mawallafa labarai a yanar gizo ta jihar Kano dake karkashin kungiyar yan jaridu ta kasa (NUJ) .

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa Kadaura24 a ranar Litinin.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Gwamna Yusuf ya bayyana zabar Dangambo a matsayin wani mataki na cigaba a fagen yada labarai na zamani.

Ya kuma yabawa shugabannin kungiyar NUJ Kano a karkashin jagorancin Kwamared Sulieman Dederi bisa nasarar kafa sabuwar kungiyar ta mawallafa labarai a yanar gizo, wanda a cewarsa hakan zai kara kaimi ga kokarin da kafafen yada labarai na gargajiya suke yi wajen inganta gaskiya da gaskiya da rikon amana.

Hukumar Shari’a ta Kano ta Gargadi Alkalai 2, ta kuma dakatar da Magatakarda 2

Gwamnan ya bayyana cewa ya na da kwarin guiwar cewa a karkashin jagorancin Dangambo, kungiyar za ta sami gagarumin ci gaba a jihar Kano da ma sauran kasashen duniya.

InShot 20250309 102403344

Ya ba da tabbacin gwamnatinsa za ta baiwa kungiyar goyon bayan da hadin kan da ake bukata domin inganta aiyukan ya’yan kungiyar.

Gwamna Yusuf ya yi wa Kwamared Dangambo da sauran Shugabannin fatan samun nasara da kuma tasiri, inda ya bukace su da su yi aiki tukuru wajen bunkasa kungiyar da inganta aikin jarida.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da nuna tallan maganin Gargajiya a Fina-finai da yawo a tituna

A wani mataki na tabbatar da bin ka'idoji tare...

Da dumi-dumi: NNPP ta nemi afuwar Tinubu kan kalaman suka da ake zargin Kwankwaso ya yi masa

  Jam’iyyar NNPP ta nemi afuwar Shugaban kasa Bola Tinubu...

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...