Daga Ibrahim Sidi Muhammad Jega.
Shugaban kwamitin aikin hajin bana a jihar Kebbi, wato Amirul Hajji, mai martaba Sarkin Kabin Argungu, Alhaji Dr. Samaila Muhammad Mera (CON), ya bukaci masu ruwa da tsaki a aikin hajjin bana da su baiwa kwamitinsa hadin kai don gudanar da Ibadar cikin nasara.
” Wannan babban aiki ne Gwannan Kebbi ya dora mana, don haka akwai bukatar kowa ya yi iya kokarinsa don mu sauke wannan nauyi da aka dora mana, ta hanyar samar da walwala ga alhazan jihar Kebbi”. Inji Sarkin Kabin Argungun.

Alhaji Samaila Mera ya bukaci hakan ne yayin zaman farko da kwamitin ya yi da hukumar Jin dadin Alhazzai ta jihar a karkashin Jagorancin Shugaban Hukumar, Alhaji Faruku Aliyu Enabo (Jagaban Gwandu).
Ya godewa gwannan jihar Kano Kwamared Nasiru Idris (kauran gwandu), tare da baiwa gwamnan tabbacin da shi da yan tawagarsa za su yi aiki tukuru don ganin ba a sami wata matsala ba tun daga nan gida Nigeria har zuwa kasa mai tsarki.
Da dumi-dumi: Sarki Aminu ya nada sabon Galadiman Kano
Da ya ke jawabin maraba, Shugaban Hukumar Jin dadin Alhazzai, Alhaji Faruku Aliyu Enabo Jagaban Gwandu, ya yi godiya da Gwamnan jihar Kebbi, a bisa cikakkiyar kulawa da ya ke baiwa hukumar, da kuma gabatar da kwamitin aikin hajjin bana cikin lokacin da ya kamata.
Jagaban Gwandu, ya bayyana cewa Hukumar zata ba da cikakken goyon baya ga kwamitin domin samun nasarar aikin Hajjin na bana.