Gwamna Abba ya Rantsar da Sabon Sakataren Gwamnatin Kano

Date:

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya jagoranci rantsar da sabon Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Alhaji Umar Farouk Ibrahim.

Da aka rantsar da sabon Sakataren a ofishinsa, gwamna Abba Kabir Yusuf ya hore shi da ya gudanar da ayyukansa bisa gaskiya da rikon amana tare da sadaukar da kai a yayin aikinsa.

InShot 20250115 195118875
Talla

Ya bayyana kwarin gwiwarsa akan sabon Sakataren gwamnatin, tare da fatan zai yi amfani da gogewarsa wajen tabbatar da kudirin gwamnatin jiha na aiwatar da ayyukan cigaba da bunkasa rayuwar al’ummar jihar Kano.

Inganta Ilimi: Abba Bichi ya dauki sabbin malamai 200 aiki

Kadaura24 ta rawaito cewa a nasa bangaren, sabon Sakataren gwamnatin jiha, Alhaji Umar Farouk Ibrahim ya yi alwashin zai bada gudunmawarsa domin daga darajar jihar Kano zuwa mataki na gaba.

Idan za a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito cewa a ranar asabar gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya bayar da sanarwar nada Farouk Umar Ibrahim a matsayin sabon sakataren gwamnatin jihar Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...