Da dumi-dumi: Kwamishina a Gwamnatin Kano ya ajiye aiki

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince da ajiye aiki da Engr. Muhammad Diggol, yayi a matsayinsa na kwamishinan ma’aikatar bibiyar aiyuka nan take.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya aikowa Kadaura24 a ranar Lahadi.

Talla

Tun a farkon mulkinsa gwama Abba Kabir Yusuf ya nada Engr. Muhammad Diggol a matsayin kwamishinan sufuri, kafin daga bisani ya saura masa wajen aiki zuwa ma’aikatar bibiyar aiyuka inda a nan ne yayi murabus .

Gwamna Yusuf ya bayyana godiyarsa ga Engr. Diggol bisa kokarinsa da jajircewarsa, sadaukarwa, da kuma bin ka’idojin aiki a lokacin da yake zama dan majalisar zartarwa ta jiha.

Gwamnan Kano ya yi sabbin nade-nade, tare da sanya ranar rantsar da sabbin kwamishinoni

A cewar sanarwar, Gwamnan ya yiwa Engr. Doggol fatan alheri a harkokin da zai sanya a gaba.

Sanarwar dai ba ta bayyana dalilin da ya sanya kwamishinan ya ajiye aikinsa ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...