Abba@62: Tabbas Kanawa za su jima suna morar Salon mulkinka – Sakon Kwankwaso ga Gwamnan Kano

Date:

Daga Sani Idris maiwaya

 

Jagoran Jam’iyyar NNPP na kasa Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya yana da salon mulkin da gwamna Abba Kabir Yusuf yake yi a Kano da irin cigaban da ya kawowa jihar.

“Babu shakka cikin watannin 19 da zamanka gwamna ka kawo wa jihar Kano cigaba mai tarin yawa a fannoni daban-daban na rayuwar al’ummar jihar, tabbas salon mulkinka abun yabo ne”.

Sanata Kwankwaso ya bayyana hakan ne a sakonsa na taya gwamna Abba Kabir Yusuf murnar cika shekaru 62 da haihuwa.

Talla

Ya ce shekaru 62 da gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi a duniya cike suke da albarka da sadukarwa musamman wajen cigaban jihar Kano da kasa baki daya.

“Salon mulkinka na sauraren koke da korafin al’ummar jihar Kano da kake mulka , ya nuna tsantsar kwarewarka wajen iya tafiyar da harkokin mulki wanda kuma haka ake bukata ga kowanne shugaba nagari”. Inji Kwankwaso

Hukumar Tace Fina-fina ta Kano ta Dakatar da Babbar Jaruma a Kannywood

Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso wanda shi ne ya yiwa Jam’iyyar NNPP takarar shugaban kasa a zaben 2023, ya yiwa gwamnan fatan samun karin shekaru masu albarka don al’umma su cigaba amfana daga gare shi .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...