Abba@62: Tabbas Kanawa za su jima suna morar Salon mulkinka – Sakon Kwankwaso ga Gwamnan Kano

Date:

Daga Sani Idris maiwaya

 

Jagoran Jam’iyyar NNPP na kasa Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya yana da salon mulkin da gwamna Abba Kabir Yusuf yake yi a Kano da irin cigaban da ya kawowa jihar.

“Babu shakka cikin watannin 19 da zamanka gwamna ka kawo wa jihar Kano cigaba mai tarin yawa a fannoni daban-daban na rayuwar al’ummar jihar, tabbas salon mulkinka abun yabo ne”.

Sanata Kwankwaso ya bayyana hakan ne a sakonsa na taya gwamna Abba Kabir Yusuf murnar cika shekaru 62 da haihuwa.

Talla

Ya ce shekaru 62 da gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi a duniya cike suke da albarka da sadukarwa musamman wajen cigaban jihar Kano da kasa baki daya.

“Salon mulkinka na sauraren koke da korafin al’ummar jihar Kano da kake mulka , ya nuna tsantsar kwarewarka wajen iya tafiyar da harkokin mulki wanda kuma haka ake bukata ga kowanne shugaba nagari”. Inji Kwankwaso

Hukumar Tace Fina-fina ta Kano ta Dakatar da Babbar Jaruma a Kannywood

Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso wanda shi ne ya yiwa Jam’iyyar NNPP takarar shugaban kasa a zaben 2023, ya yiwa gwamnan fatan samun karin shekaru masu albarka don al’umma su cigaba amfana daga gare shi .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...