Gobara ta tashi a Gidan da Ganduje ya Koma makonni biyu da suka gabata

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Gobara ta tashi a gidan da gwamnan jihar Kano mai barin gado, Abdullahi Umar Ganduje, ya koma makonni biyu da suka gabata.

 

Majiyar Kadaura24 SOLACEBASE Gobarar dai ta tashi ne da yammacin ranar Litinin, in da ta kone kaya na miliyoyin Naira.

Da dumi-dumi: Ganduje ya mika muhimman bayanan gwamnatin Kano ga Abba Gida-gida

Gidan Gandujen dai na nan akan titin Miagun, bayan Kano Club, a unguwar Nasarawa GRA Kano.

Akwai masu shirin tayar da hatsaniya a lokacin rantsar da sabbin gwamnatoci a Najeria – DSS

Jaridar ta ce majiya mai tushe ta shaida mata cewa, gobarar ta kone sashin da ake kiwon shanu da sauran dabbobi kuma da yawa daga cikin dabbobin sun mutu.

 

Da aka tuntubi babban sakataren yada labaran gwamnan, Abba Anwar, ya ce ba ya gari, don haka ba shi da masaniyar faruwar lamarin.

Sai dai jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Kano, Saminu Yusuf, ya tabbatar da tashin gobarar.

Ya kuma ce an shawo kanta a lokacin da jami’ansu suka isa gidan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...