Gobara ta tashi a Gidan da Ganduje ya Koma makonni biyu da suka gabata

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Gobara ta tashi a gidan da gwamnan jihar Kano mai barin gado, Abdullahi Umar Ganduje, ya koma makonni biyu da suka gabata.

 

Majiyar Kadaura24 SOLACEBASE Gobarar dai ta tashi ne da yammacin ranar Litinin, in da ta kone kaya na miliyoyin Naira.

Da dumi-dumi: Ganduje ya mika muhimman bayanan gwamnatin Kano ga Abba Gida-gida

Gidan Gandujen dai na nan akan titin Miagun, bayan Kano Club, a unguwar Nasarawa GRA Kano.

Akwai masu shirin tayar da hatsaniya a lokacin rantsar da sabbin gwamnatoci a Najeria – DSS

Jaridar ta ce majiya mai tushe ta shaida mata cewa, gobarar ta kone sashin da ake kiwon shanu da sauran dabbobi kuma da yawa daga cikin dabbobin sun mutu.

 

Da aka tuntubi babban sakataren yada labaran gwamnan, Abba Anwar, ya ce ba ya gari, don haka ba shi da masaniyar faruwar lamarin.

Sai dai jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Kano, Saminu Yusuf, ya tabbatar da tashin gobarar.

Ya kuma ce an shawo kanta a lokacin da jami’ansu suka isa gidan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abubakar Bichi ya bada gudumawar motocin bas 13 ga jami’o’in Kano da taraktoci 11 ga yan mazabarsa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Dan Majalisar tarayya mai wakiltar karamar...

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...