Gobara ta tashi a Gidan da Ganduje ya Koma makonni biyu da suka gabata

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Gobara ta tashi a gidan da gwamnan jihar Kano mai barin gado, Abdullahi Umar Ganduje, ya koma makonni biyu da suka gabata.

 

Majiyar Kadaura24 SOLACEBASE Gobarar dai ta tashi ne da yammacin ranar Litinin, in da ta kone kaya na miliyoyin Naira.

Da dumi-dumi: Ganduje ya mika muhimman bayanan gwamnatin Kano ga Abba Gida-gida

Gidan Gandujen dai na nan akan titin Miagun, bayan Kano Club, a unguwar Nasarawa GRA Kano.

Akwai masu shirin tayar da hatsaniya a lokacin rantsar da sabbin gwamnatoci a Najeria – DSS

Jaridar ta ce majiya mai tushe ta shaida mata cewa, gobarar ta kone sashin da ake kiwon shanu da sauran dabbobi kuma da yawa daga cikin dabbobin sun mutu.

 

Da aka tuntubi babban sakataren yada labaran gwamnan, Abba Anwar, ya ce ba ya gari, don haka ba shi da masaniyar faruwar lamarin.

Sai dai jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Kano, Saminu Yusuf, ya tabbatar da tashin gobarar.

Ya kuma ce an shawo kanta a lokacin da jami’ansu suka isa gidan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...