Ba zan baiwa ‘yan Nigeria Kunya ba – Tinubu

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Zababben shugaban kasa, Bola Tinubu, ya sha alwashin ba zai baiwa ‘yan Najeriya kunya ba.

 

Tinubu ya bayyana haka ne bayan da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya karrama shi da lambar girmamawa ta kasa (GCFR) a fadar shugaban kasa da ke Abuja ranar Alhamis.

 

Ya ce ya fahimci karramawar da Kuma aikin da ke gabansa, inda ya yi alkawarin ba zai baiwa shugaban kasa da ‘yan Nijeriya kunya ba.

 

“Ni mutum ne mai saukin kai wanda ya ci gajiyar goyon baya da fatan alkhairin al’ummar Najeriya. Jama’a sun dogara gare mu, Ka yi aikinka nima zan yi nawa don inganta rayuwar al’ummar Nigeria .

“Idan na shigo faggen dole ne na yi abun da ya dace wajen inganta fannin tsaro, tattalin arziki, noma, ayyuka, ilimi, lafiya da wutar lantarki da kuma sauran bangarori , ya mai girma Shugaban kasa da kai da yan Nigeria dole ne in yaba muku in kuma fidda ku kunya.”

Ya godewa Buhari bisa karramawar da ya yi masa da kuma mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, wanda ya samu kambun babban kwamandan Niger (GCON).

Ya kara da cewa sadaukarwar da Shugaban kasa ya yi na samar da kyakkyawan shugabanci ga dimokuradiyya ba abu ne mai sauƙi ba.

Tinubu ya kuma yaba wa shugaba Buhari bisa karrama marigayi MKO Abiola, wanda ya lashe zaben shugaban kasa da aka soke ranar 12 ga watan Yunin 1993.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...