Babu Mai laifin da zamu bari – Buhari

Date:

Daga Surayya Abdullah Tukuntawa

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya nuna bacin ransa kan kisan kiyashin da ake yi wa ‘yan kasar nan, ciki har da shugaban ‘yan sintiri da kuma shugaban Dabna, a kauyen Dugwaba da ke karamar hukumar Hong a Jihar Adamawa.

Shugaban yana mayar da martani ne kan abin da ya faru a ranar Laraba, yana cewa, “Yadda ake nuna rashin imani da rashin tausayi ba za mu bari duk mai hannu ya tafi haka ba, duk wani mai laifi sai mun hukunta shi”.

A wata sanarwa da mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai ga shugaban, Garba Shehu ya fitar shugaban ya bai wa jami’an tsaro umarnin “Su ninka kokarinsu da kuma matakan da suke dauka kan wadannan bata gari cikin gaggawa”.

Buhari ya kuma umarci ma’aikatar ba da agaji da ta duba abin da aka yi asara a yankin a kuma aika musu da taimakon gaggawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...

Al’ummar Kano ku baiwa AA Zaura hadin Kai domin ya kawo karshen fadan Daba – Baba Yawale

Daga Halima Umar Dogo   Babban Hadimin AA Zaura Alhaji Baba...

Gwamnatin Kano ta magantu kan Hukuncin kotu na zaben kananan hukumomi

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Kano ta bayyana farin...