Ganduje ya nada Wanda Zai Gaji Muhuyi Magaji a Hukumar yaki da rashawa ta Kano

Date:

Daga Amira Sanusi


Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na jihar Kano ya amince da nadin Barista Mahmoud Balarabe, wanda a halin yanzu shi ne Darakta na Mai lura da shigar da kara na Ma’aikatar Shari’a ta jihar, a matsayin mukaddashin Shugaban Hukumar karbar karbar korafe-karafe da yaki da Cin Hanci da Rashawa ta jihar Kano.


Sanarwar nadin na dauke ne Cikin wata sanarwa da Babban Sakataren yada labaran gwamna Malam Abba Anwar ya aikowa Kadaura24.


 Sanarwar nadin ta fara aiki nan take kuma Gwamna Ganduje ya umarci mukaddashin Shugaban Hukumar da ya gudanar da ayyukansa yadda ya kamata, bisa ga tsarin da dokar da aka kafa Hukumar akai

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...