Babu Mai laifin da zamu bari – Buhari

Date:

Daga Surayya Abdullah Tukuntawa

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya nuna bacin ransa kan kisan kiyashin da ake yi wa ‘yan kasar nan, ciki har da shugaban ‘yan sintiri da kuma shugaban Dabna, a kauyen Dugwaba da ke karamar hukumar Hong a Jihar Adamawa.

Shugaban yana mayar da martani ne kan abin da ya faru a ranar Laraba, yana cewa, “Yadda ake nuna rashin imani da rashin tausayi ba za mu bari duk mai hannu ya tafi haka ba, duk wani mai laifi sai mun hukunta shi”.

A wata sanarwa da mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai ga shugaban, Garba Shehu ya fitar shugaban ya bai wa jami’an tsaro umarnin “Su ninka kokarinsu da kuma matakan da suke dauka kan wadannan bata gari cikin gaggawa”.

Buhari ya kuma umarci ma’aikatar ba da agaji da ta duba abin da aka yi asara a yankin a kuma aika musu da taimakon gaggawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano za ta sake gina Masallacin da aka kona a Gezawa

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin gwamna...

Hukumar shari’a ta Kano ta ladaftar da wasu ma’aikatan kotu

Daga Usman Hamza   Hukumar Kula da Harkokin shari'a ta Jihar...

2027: Malam Shekarau ya bayyana matsayar kungiyarsu kan hadakar yan hamayya a Nigeria

Ƙungiyar siyasa ta Northern Democrats, ƙarƙashin jagorancin Malam Ibrahim...

Da Ɗumi-Ɗumi: Dangote ya sake rage farashin man fetur

Matatar man fetur ta Dangote ta sanar da ƙarin...