Kwacen waya: Ya kamata gwamnatin Kano da hukumomin tsaro su tashi tsaye – Auwal Danlarabawa

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Kungiyar Grassroot Care and Aid Foundation ta nemi Gwamnatin Jihar Kano da hukumomin tsaro su gaggauta ɗaukar mataki kan yawaitar matsalar kwacen waya da fadace-fadacen daba da ke jefa rayukan al’umma cikin haɗari.

Kadaura24 ta rawaito wannan na cikin wata wasika da shugaban ƙungiyar, Amb. Auwalu Muhammad Danlarabawa, ya aike wa Kwamishinan Harkokin Tsaro da sauran hukumomin tsaro na jihar, a ranar Asabar, 14 ga Yuni, 2025.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Kungiyar ta bayyana damuwa kan yadda matasa da mata da sauran marasa ƙarfi ke fuskantar barazana daga masu aikata laifuka, musamman a yankunan da aka fi samun fadace-fadacen daba da kwacen waya.

Dawo da Gwadabe ya Jagoranci Anti Daba Hanya ce ta Magance Fadan Daba a Kano

Ta bukaci a ƙara yawan sintiri da sa ido a wuraren da abin ya fi kamari, da kuma ƙarfafa dabarun tattara bayanan sirri tare da haɗin gwiwa da shugabannin al’umma da ƙungiyoyin matasa domin dawo da zaman lafiya.

InShot 20250309 102403344

Kungiyar ta kuma yaba da kokarin da hukumomin tsaro ke yi, tare da ƙarfafa gwiwarsu wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...