Sarki Aminu Ado Bayero ya fara daukar matakan gudanar da Hawan Sallah Karama a Kano

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Mai martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero ya sanar da rundunar ‘yan sandan jihar Kano shirin sa na gudanar da hawan Sallah karama .

A wata wasika da jaridar Kadaura24 ta gani, Sakataren Sarkin Abdullahi Haruna Kwaru ne ya sanar da kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano da Hukumar DSS da ta Civil defense cewa Sarkin ya kammala shirye-shiryen gudanar da bikin, wanda zai gudana a karshen watan Maris na 2025.

InShot 20250309 102403344
Talla

Kamar yadda wasikar ta nuna, za a gudanar da bukukuwan Hawan Sallar Idi, da Hawan Daushe, da Hawan Nassarawa a ranakun 1, 2, da 3 ga watan Shawwal 1446, sannan a yi bikin al’adu a rana ta hudu.

Wasikar ta Kwaru ta nuna cewa, a bana za su hade bikin cikar Sarkin shekaru biyar a kan karagar magabatansa.

“Makasudin wannan wasiƙar ita ce sanar da hukumomin tsaro a Jihar Kano, musamman rundunar ‘yan sanda a hukumance, cewa bikin Sallah na bana ya zo daidai da cika shekaru biyar (5) da Mai Martaba ya yi a kan karagar mulkin magabatansa, tare da ba da tabbacin cewa za a gudanar da dukkan bukukuwan cikin lumana.” a cewar wasikar.

2027: Shekarau ya Caccaki hadakar Atiku da El-Rufai da Obi

Ya bayyana fatan a gudanar da bukukuwan lami lafiya tare da addu’ar neman kariya, koshin lafiya, da zaman lafiya a tsakanin al’umma.

Ofishin Sarkin ya nemi hadin kan hukumomin tsaro don tabbatar da an gudanar da bukukuwan kwanciya hankali da lumana kuma cikin nasara.

Haka kuma a wata sanarwa da sakataren yada labaran Sarkin Abubakar Balarabe kofar Na’isa ya fitar ya bukaci al’ummar Musulmi da su fita domin ganin yadda Sarkin za gudanar da bukukuwan sallah karama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hawan Sallah: Yansandan Kano sun gayyaci hadimin Sarki Sanusi II bayan mutuwar wani

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta...

Barka da Sallah: Gwamnan Kano ya bukaci yan jihar su rungumi zaman lafiya da adalci

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Sarki Aminu da Sarki Sanusi sun bukaci gwamnati ta hukunta duk masu hannu a kisan Mafarautan Kano a Edo

Daga Aliyu Danbala Gwarzo da Sani Idris maiwaya   Mai Martaba...

Murtala Sule Garo ya yiwa Kanawa Barka da Sallah

Ina taya daukacin al’ummar Musulmi maza da mata musamman...