Sarki Aminu da Sarki Sanusi sun bukaci gwamnati ta hukunta duk masu hannu a kisan Mafarautan Kano a Edo

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo da Sani Idris maiwaya

 

Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero da Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi II sun yi kira ga Gwamnati ta tabbatar ta dauki matakin hukunta duk wadanda aka samu da laifin kisan mafarauta yan asalin jihar Kano Wanda akayi a jihar Edo.

Sarakunan sun yi wannan kira ne a sakonsu na Barka da Sallah, tare da jaje da ta’aziyyar rasuwar yan asalin jihar Kano da aka kashe a jihar Edo.

Murtala Sule Garo Ya Taya Al’ummar Musulmi Barka da Sallah

Sun yi Allah -wadai da kisan sannan su ka yi addu’ar Allah ya jikan mamatan ya kuma gafarta musu ya karbi shadarsu.

InShot 20250309 102403344
Talla

Sarkin Kano ya bukaci Gwamnati a kowane mataki da ta samar da hanyoyin saukakawa jama’a sakamakon wahalhalun rayuwa da al’uma ke fama.

IMG 20250330 WA0005
Sakon Barka da Sallah

A wani sako da sakataren yada labaran Sarki Aminu, Abubakar Balarabe kofar Na’isa ya ce Aminu Ado Bayero ya sake tunatar da Gwamnati irin nauyin da yake kanta na kare rayuka da dukiyoyin al’umma da kuma lafiyarsu.

Ya bukaci mawadata dake cikin al’uma su cigaba da taimakon da tallafawa marasa karfi domin samun saukin al’amuran rayuwa na yau da kullum.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...

Tinubu ka fadawa yan Nigeria Inda ka tsaya har kwana 5 bayan taron BRICS – ADC

    Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC ta soki Shugaban...

Da dumi-dumi: Yadda akai Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami'an tsaro a Nigeria...