Murtala Sule Garo Ya Taya Al’ummar Musulmi Barka da Sallah

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Tsohon mataimakin dan takarar gwamna na jam’iyyar APC a jihar Kano, Hon. Murtala Sule Garo ya bukaci al’ummar Musulmi da su ci gaba da dagewa wajen yin ibadu ko da bayan azumin watan Ramadan.

Garo ya bayyana haka ne a cikin sakonsa na Barka da Sallah da ya aikowa Kadaura24 ranar Asabar a Kano.

Ya taya al’ummar musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan na shekarar 2025 cikin nasara da kuma bukukuwan Sallah.

InShot 20250309 102403344
Talla

Galadima Garo ya tunatar da al’umma cewa su cigaba da aiki koyarwar Alkur’ani da Hadisi domin yin hakan zai sake kyuatata zaman lafiya da soyayyar juna da samun yardar Allah S W A.

Ya ce kamata ya yi mutane su dore da yadda su ka rika yin ibadu a cikin watan azumin Ramadan, har tsawon rayuwarsu.

Sallah: Kungiyar RATTAWU a Kano ta sauke kabakin arziki ga yayanta

Da yake godewa Allah da ya nuna masa wannan lokacin, tsohon kwamishinan kananan hukumomi da masarautu, Murtala Sule Garo, ya bayyana cewa bikin sallah ya ta’allaka ne da soyayya, tallafawa mabukata da kuma zaman lafiya da yin abubuwan da ba su sabawa koyarwar addinin musulunci ba.

Garo ya bukaci al’ummar musulmi da su yi amfani da lokutan bukukuwan Sallah domin su yi addu’o’in samun dawwamammen zaman lafiya a Kano da Najeriya baki daya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...

Tinubu ka fadawa yan Nigeria Inda ka tsaya har kwana 5 bayan taron BRICS – ADC

    Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC ta soki Shugaban...

Da dumi-dumi: Yadda akai Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami'an tsaro a Nigeria...