2027: Shekarau ya Caccaki hadakar Atiku da El-Rufai da Obi

Date:

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Ibrahim Shekarau, ya bayyana cewa babu wata haɗakar ‘yan siyasa da za ta iya sauke Shugaba Bola Tinubu da jam’iyyar APC mai mulki a zaɓen 2027.

Matsayar Shekarau na zuwa ne kasa da sa’o’i 48 bayan wasu manyan ‘yan siyasa daga jam’iyyun adawa, ciki har da tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, da ɗan takarar shugabancin ƙasa a jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, suka soki matsayar Gwamnatin Tarayya game da rikicin siyasa a Jihar Ribas a wani taron manema labarai da suka gudanar a Abuja.

InShot 20250309 102403344
Talla

A wata sanarwa da Dr. Sule Yau ya fitar a madadin Shekarau, ya jaddada cewa, sabanin abin da wasu ke hasashe, wannan haɗaka kawai wata tarayya ce ta masu niyyar tsayawa takarar shugaban ƙasa ko mataimakin shugaban ƙasa, kuma babu wanda daga cikin jagororin wannan haɗaka da ya tuntubi shugabancin jam’iyyarsa.

Sanatan ya bayyana haɗakar a matsayin wata hadin guiwa ta wasu gungun mutane kawai, yana mai cewa, ko da suna da manyan sunaye, hakan ba ya nufin sun haɗe wuri guda domin zama jam’iyya guda ba.

Cin zarafi: Gwamnatin Kano za ta sanya kafar wando da sojojin baka – Kwamared Waiya

A cewarsa, “Haɗakar wasu manyan jiga-jigai daga jam’iyyun adawa abu ne mai kyau, kamar yadda aka gani kwanan nan a ƙarƙashin abin da suke kira ‘coalition’ na jam’iyyun adawa.

“Babu ɗaya daga cikin manyan jagororin da ke tafe da shugabancin jam’iyyarsa. Kuma wannan taron wasu gungun mutane, duk da suna da manyan sunaye, ba za a kira shi ‘merger’ ba, domin a bisa doka, sai jam’iyyun da aka rijista ne kawai za su iya yin cikakken haɗaka.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Buhari: Majalisar Nigeria ta dakatar da duk aiyukanta

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Majalisar dokokin Nigeria ta dage zamanta...

Gwamnati ta baiwa ma’aikata hutu saboda rasuwar Muhammad Buhari

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Katsina karkashin gwamna Umar...

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...