Yanzu-yanzu: Tinubu ya aiyana dokar ta baci a jihar Rivers

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya aiyana dokar ta baci a jihar Rivers.

Idan za a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito ana ta rikicin Shugabanci a jihar Rivers, yayin da ake samu rashin jituwa tsakanin gwamnatin jihar da bangaren majalisar dokokin jihar.

InShot 20250309 102403344
Talla

Shugaban kasar ya aiyana dokar ne bayan wata ganawa da yayi da shugabannin hukumomin tsaron kasar kan rikicin jihar ta Rivers.

Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Hukuncin Kotu

Yanzu haka dai za a iya cewa ba gwamnati a jihar har sai matakin da shugaban kasar ya dauka .

Rahotannin sun tabbatar da cewa shugaban kasar ya dakatar da gwamnatin jihar da dukkanin yan majalisar dokokin jihar har na tsahon watanni shida.

Shugaban kasar ya kuma nada  Vice Admiral Ibok Ete Ibas a matsayin mai rikon mukamin gwamnan Rivers State.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Amfani da al’ada a cikin fina-finan kannywood ne ya hana masa’antar ci gaba – Khadija Osi

Jaruma a masana'antar Kannywood Khadija Muhammad wacce aka fi...

Nasarar da Ɗaliban Kano suka Samu a NECO Kokari ne na Gwamnatin Ganduje – Sanusi Kiru

Tsohon Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Hon. Muhammad Sanusi...

Gwamnatin Tarayya ta Kaddamar da Aikin samar da wutar sola na Naira Biliyan 12 a asibitin Malam Aminu Kano

Kwana biyu bayan rikicin wutar lantarki tsakanin Asibitin Koyarwa...

Kano Ta Zama Zakara A Jarrabawa NECO Ta Bana

Hukumar shirya jarrabawar kammala sakandire ta Najeriya (NECO),ta fitar...