Daga Rukayya Abdullahi Maida
Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano kuma Babban Lauyan Gwamnati, Haruna Isa Dederi, ya bayyana cewa hukuncin da Kotun Daukaka Kara, reshen Abuja, ta yanke kan takaddamar sarauta bai soke mayar da Muhammadu Sanusi II a matsayin Sarkin Kano na 16 ba.
Da ya ke jawabi ga manema labarai, Dederi ya jaddada cewa hukuncin Kotun Daukaka Kara na ranar 10 ga Janairu, 2025, ya tabbatar da ikon gwamnatin jihar na mayar da Sanusi kan karagar mulki.
Ya bayyana cewa kawai Kotun Koli ce ke da ikon sauya wannan hukunci.

Maganganunsa sun biyo bayan hukuncin da kotun ta yanke kan bukatar dakatar da aiwatar da hukuncin da Aminu Baba DanAgundi, daya daga cikin masu nada sarki masu biyayya ga Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, ya shigar.
Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci
Kotun ta umarci a ci gaba da tsayawa a inda ake har sai Kotun Koli ta yanke hukunci na karshe.
Dederi ya sake nanata cewa kotun daukaka kara ba ta soke hukuncinta na baya ba, sai dai kawai ta dakatar da aiwatar da shi har sai Kotun Koli ta yanke hukunci.