Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Hukuncin Kotu

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano kuma Babban Lauyan Gwamnati, Haruna Isa Dederi, ya bayyana cewa hukuncin da Kotun Daukaka Kara, reshen Abuja, ta yanke kan takaddamar sarauta bai soke mayar da Muhammadu Sanusi II a matsayin Sarkin Kano na 16 ba.

Da ya ke jawabi ga manema labarai, Dederi ya jaddada cewa hukuncin Kotun Daukaka Kara na ranar 10 ga Janairu, 2025, ya tabbatar da ikon gwamnatin jihar na mayar da Sanusi kan karagar mulki.

Ya bayyana cewa kawai Kotun Koli ce ke da ikon sauya wannan hukunci.

InShot 20250309 102403344
Talla

Maganganunsa sun biyo bayan hukuncin da kotun ta yanke kan bukatar dakatar da aiwatar da hukuncin da Aminu Baba DanAgundi, daya daga cikin masu nada sarki masu biyayya ga Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, ya shigar.

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

Kotun ta umarci a ci gaba da tsayawa a inda ake har sai Kotun Koli ta yanke hukunci na karshe.

Dederi ya sake nanata cewa kotun daukaka kara ba ta soke hukuncinta na baya ba, sai dai kawai ta dakatar da aiwatar da shi har sai Kotun Koli ta yanke hukunci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Yusuf ya taya Dangambo murnar zama shugaban kungiyar mawallafa labarai ta internet na Kano

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Hajjin bana: Za mu yi duk abun da ya dace don kyautata walwalar alhazan Jihar Kebbi – Amirul Hajji

Daga Ibrahim Sidi Muhammad Jega.   Shugaban kwamitin aikin hajin bana...

Bayan dawo da Gwadabe Anti daba, Yansanda sun kama yan daba 33 a Kano

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar Yansanda ta Kasa reshen jihar...

Sabon Rikici ya Barke a Jam’iyyar NNPP ta Karamar Hukumar Dawakin Tofa

Rikici ya barke a cikin jam’iyyar NNPP ta karamar...