Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Hukuncin Kotu

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano kuma Babban Lauyan Gwamnati, Haruna Isa Dederi, ya bayyana cewa hukuncin da Kotun Daukaka Kara, reshen Abuja, ta yanke kan takaddamar sarauta bai soke mayar da Muhammadu Sanusi II a matsayin Sarkin Kano na 16 ba.

Da ya ke jawabi ga manema labarai, Dederi ya jaddada cewa hukuncin Kotun Daukaka Kara na ranar 10 ga Janairu, 2025, ya tabbatar da ikon gwamnatin jihar na mayar da Sanusi kan karagar mulki.

Ya bayyana cewa kawai Kotun Koli ce ke da ikon sauya wannan hukunci.

InShot 20250309 102403344
Talla

Maganganunsa sun biyo bayan hukuncin da kotun ta yanke kan bukatar dakatar da aiwatar da hukuncin da Aminu Baba DanAgundi, daya daga cikin masu nada sarki masu biyayya ga Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, ya shigar.

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

Kotun ta umarci a ci gaba da tsayawa a inda ake har sai Kotun Koli ta yanke hukunci na karshe.

Dederi ya sake nanata cewa kotun daukaka kara ba ta soke hukuncinta na baya ba, sai dai kawai ta dakatar da aiwatar da shi har sai Kotun Koli ta yanke hukunci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Dangote ya rage farashin man fetur a Nigeria

Matatar mai ta dangote ta rage farashin man fetur...

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...