Ban San Taulaci ba Sai da na Zama Sarkin Kano – Sarki Sanusi II

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi II, ya ce sai da ya zama Sarkin Kano sannan ya san hakikanin talauci .

Sarki Sanusi ya bayyana haka yayin laccar da aka shirya gabanin bikin cikar tsohon gwamnan jihar Ribas, Rotimi Amaechi, shekaru 60 a Abuja, ranar Asabar.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Tsohon Gwamnan na CBN ya ce, “Da yawa daga cikin Manya a Najeriya ba su san mene ne talauci ba, a matsayina na masanin tattalin arziki, tsohon Gwamnan CBN, ina ganin adadin matalauta, Amma ban san hakikanin talaucin ba sai da na zama sarki.

Iftila:I: Gwamnatin Kano ta Aiyana Ranar Litinin a Matsayin Ranar Hutu
“Kuma ka je kauye ka ga ruwan da suke sha, da gidajen da suke rayuwa a ciki, da kuma irin ajujuwan da suke Karatu a ciki wadanda ko rufi ba su da shi”. Inji Sarki Sanusi.

InShot 20250309 102403344

Muna cikin matsalar da ya kamata mu gyara ta fa, saboda dukkanin mu Muna rayuwa a birane, su kuma talakawa sun rayuwa cikin mawuyacin hali da ya kamata mu Kai musu dauki don inganta rayuwarsu

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dan Majalisar tarayya daga Kano ya fice daga jam’iyyar NNPP

Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Kano Municipal, Injiniya Sagir...

Abin mamaki: Barawo ya sace Motar dake cikin ayarin motocin gidan gwamnatin Kano

Wani barawon mota ya kutsa cikin gidan gwamnatin jihar...

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...