Gwamnan Kano ya Bayyana Matsayarsa Game da Hawan Sallah Karama a Jihar

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi alkawarin baiwa sarakunan Kano da hakimai dukkanin goyon bayanl da gudunmawar da su ke bukata domin gudanar da hawan sallah karama.

” Shi mutumin kano babu abun da yake so bayan kammala azumin watan Ramadana,illa sallah ta zo ya caba ado ya fito domin ya gaishe da Sarkinsa , shi kuma Sarkin ya yi masa addu’a”.

Gwamna Abba Kabir Yusuf na wannan jawabi ne yayin da yake gabatar da shan ruwa da sarakunan a fadar gwamnatin a yau talata .

InShot 20250309 102403344
Talla

Gwamnan ya ce yana kira ga sarakunan Kano Rano Gaya da Karaye da su da hakimansu da su fito domin gudanar da bukukuwa hawan sallah kamar yadda aka saba.

Yanzu-yanzu: Tinubu ya aiyana dokar ta baci a jihar Rivers

Idan za a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito a shekarar da ta gabata da Babbar sallah ba a gudanar da hawan sallah a Kano ba , saboda rikicin Masarautar Kano da yanzu haka yake gaban Kotu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da nuna tallan maganin Gargajiya a Fina-finai da yawo a tituna

A wani mataki na tabbatar da bin ka'idoji tare...

Da dumi-dumi: NNPP ta nemi afuwar Tinubu kan kalaman suka da ake zargin Kwankwaso ya yi masa

  Jam’iyyar NNPP ta nemi afuwar Shugaban kasa Bola Tinubu...

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...