Daga Rukayya Abdullahi Maida
Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya aiyana dokar ta baci a jihar Rivers.
Idan za a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito ana ta rikicin Shugabanci a jihar Rivers, yayin da ake samu rashin jituwa tsakanin gwamnatin jihar da bangaren majalisar dokokin jihar.

Shugaban kasar ya aiyana dokar ne bayan wata ganawa da yayi da shugabannin hukumomin tsaron kasar kan rikicin jihar ta Rivers.
Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Hukuncin Kotu
Yanzu haka dai za a iya cewa ba gwamnati a jihar har sai matakin da shugaban kasar ya dauka .
Rahotannin sun tabbatar da cewa shugaban kasar ya dakatar da gwamnatin jihar da dukkanin yan majalisar dokokin jihar har na tsahon watanni shida.
Shugaban kasar ya kuma nada Vice Admiral Ibok Ete Ibas a matsayin mai rikon mukamin gwamnan Rivers State.