Gwamna Abba ya Rantsar da Sabon Sakataren Gwamnatin Kano

Date:

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya jagoranci rantsar da sabon Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Alhaji Umar Farouk Ibrahim.

Da aka rantsar da sabon Sakataren a ofishinsa, gwamna Abba Kabir Yusuf ya hore shi da ya gudanar da ayyukansa bisa gaskiya da rikon amana tare da sadaukar da kai a yayin aikinsa.

InShot 20250115 195118875
Talla

Ya bayyana kwarin gwiwarsa akan sabon Sakataren gwamnatin, tare da fatan zai yi amfani da gogewarsa wajen tabbatar da kudirin gwamnatin jiha na aiwatar da ayyukan cigaba da bunkasa rayuwar al’ummar jihar Kano.

Inganta Ilimi: Abba Bichi ya dauki sabbin malamai 200 aiki

Kadaura24 ta rawaito cewa a nasa bangaren, sabon Sakataren gwamnatin jiha, Alhaji Umar Farouk Ibrahim ya yi alwashin zai bada gudunmawarsa domin daga darajar jihar Kano zuwa mataki na gaba.

Idan za a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito cewa a ranar asabar gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya bayar da sanarwar nada Farouk Umar Ibrahim a matsayin sabon sakataren gwamnatin jihar Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwankwaso ya caccaki gwamnatin Tinubu

  Tsohon gwamnan jihar Kano, Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso ya...

Yanzu-yanzu: Jam’iyyar APC ta yi Sabon Shugabanta na Kasa

  Ministan Jinkai da ba da Agajin Gaggawa, Farfesa Nentawe...

Ku shiga harkokin Kasuwanci domin akwai albarka a ciki – Sarkin Kabin Jega ga matasa

Daga: Ibrahim Sidi Mohammad Jega Sarkin Kabin Jega, Alhaji Muhammad...

Kotua a Kano ta yankewa G-Fresh hukuncin zaman gidan yari

Kotu ta aike daAbubakar Ibrahim G. Fresh gidan gyaran...