Inganta Noma: Sanata Barau zai tallafawa Matasa 558 daga Arewa maso yammacin Nigeria

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa
Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata Barau Jibrin ya bayyana kudirnsa na tallafawa matasa 558 da suka fito daga yankin arewa maso yammacin Nigeria da tallafin Naira Biliyan 2 don inganta harkokin noma a yankin.
Sanata Barau Jibrin ya zai ba da tallafin ne a karkashin wani shiri mai taken: Barau Initiative for Agricultural Revolution in the North West (BIARN), za a zabo matasa manoma uku daga kowace kananan hukumomi 186 na jihohi bakwai da suka kunshi shiyyar Arewa maso da suka haɗar da Kano, Kaduna, Katsina, Kebbi, Jigawa, Sokoto da Zamfara.
InShot 20250115 195118875
Talla
Ya ce duk wanda ya yi nasara a shirin zai samu Naira miliyan 5 don yin noma a wannan kakar, kuma kimanin Naira biliyan 2.79 za a raba wa matasan da suka yi nasara.
Sanata Barau, ya ce an kirkiri wannan shiri ne domin bunƙasa harkar noma domin samun wadatar abinci kamar yadda shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya gabatar da sabon tsarin haɓaka noma don samar da abinci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugaban K/H Garun Mallam zai Raba Audugar Mata 500 ga Makarantun Sakandiren Matan yankin

Daga Safiyanu Dantala Jobawa Shugaban karamar hukumar garun mallam Aminu...

Kwamitin Majalisar Wakilai ya gabatar da shawarar kara Jihohi 31 a Nigeria

Daga Maryam Muhammad Ibrahim Kwamitin majalisar wakilan Nigeria mai kula...

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...