Inganta Noma: Sanata Barau zai tallafawa Matasa 558 daga Arewa maso yammacin Nigeria

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa
Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata Barau Jibrin ya bayyana kudirnsa na tallafawa matasa 558 da suka fito daga yankin arewa maso yammacin Nigeria da tallafin Naira Biliyan 2 don inganta harkokin noma a yankin.
Sanata Barau Jibrin ya zai ba da tallafin ne a karkashin wani shiri mai taken: Barau Initiative for Agricultural Revolution in the North West (BIARN), za a zabo matasa manoma uku daga kowace kananan hukumomi 186 na jihohi bakwai da suka kunshi shiyyar Arewa maso da suka haɗar da Kano, Kaduna, Katsina, Kebbi, Jigawa, Sokoto da Zamfara.
InShot 20250115 195118875
Talla
Ya ce duk wanda ya yi nasara a shirin zai samu Naira miliyan 5 don yin noma a wannan kakar, kuma kimanin Naira biliyan 2.79 za a raba wa matasan da suka yi nasara.
Sanata Barau, ya ce an kirkiri wannan shiri ne domin bunƙasa harkar noma domin samun wadatar abinci kamar yadda shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya gabatar da sabon tsarin haɓaka noma don samar da abinci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Dangote ya rage farashin man fetur a Nigeria

Matatar mai ta dangote ta rage farashin man fetur...

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...