Farfesa Gwarzo ya taya Gwamnan Kano murnar cika Shekaru 62 A Duniya, ya bayyana shi a matsayin shugaban nagari

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Shugaban rukunin jami’o’in MAAUN Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo ya taya Gwamna Abba Kabir Yusuf murnar cika shekaru 62 da haihuwa, inda ya bayyana shi a matsayin shugaba mai hangen nesa wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen yi wa al’umma hidima.

A wata sanarwa da ya sanya wa hannu, Farfesa Gwarzo ya ce “Dukkan godiya ta tabba ga Allah Madaukakin Sarki da ya raya mu cikin koshin lafiya har muka shaida wannan gagarumin biki na murnar zagayowar ranar haihuwarka.”

Talla

Manyan nasarorin da ka samu ya zuwa yanzu a fannonin ilimi, lafiya, da samar da ababen more rayuwa ya nuna yadda kake da kishi da son ci gaban jihar Kano.

Abba@62: Tabbas Kanawa za su jima suna morar Salon mulkinka – Sakon Kwankwaso ga Gwamnan Kano

“Ya kamata sauran gwamnoni kasar nan su yi koyi da yadda kake sadaukar da kai don hidimtawa al’ummar Kano, lallai tarihi zai da dade yana tunawa da hidimar da ka yi wa Kano. Tabbas Kano ta yi sa’ar samun ka a matsayin gwamna.” Inji Farfesa Gwarzo

Farfesa Gwarzo wanda shi ne wanda ya assasa Jami’ar Maryam Abacha American University of Nigeria, Niger, Franco-British International University Kaduna da Canada University of Nigeria da ke Abuja ya yi addu’ar Allah Madaukakin Sarki ya yi wa gwamna jagora wajen sauke nauyin da ke kansa, ya kuma kara masa basira da koshin lafiya domin ya cigaba da hidimtawa al’umma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...