Zaɓen kananan hukumomi: Gwamnatin Kano ta Sanya Dokar takaita zirga-zirga

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Gwamnatin Kano ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon sa’o’i 18 daga ƙarfe 12:00 na daren yau Juma’a zuwa 6:00 na yammacin gobe Asabar.

Gwamnatin ta ayyana dokar ce bayan tuntuɓar hukumomin tsaro kamar yadda wata sanarwa da Kwamishinan Labarai da Harkokin Cikin Gida, Baba Halilu Dantiye ya fitar a yammacin wannan Juma’ar.

Talla

Baba Dantiye ya buƙaci jama’a da su mutunta wannan doka ta taƙaita zirga-zirga domin bayar da haɗin kai wajen tabbatar da an gudanar da zaɓen ƙananan hukumomin jihar cikin aminci.

Ba fashi za mu gudanar da zaben kananan hukumomin Kano gobe Asabar. KANSIEC

Kwamishinan ya nanata ƙudirin gwamnatin na tabbatar da an gudanar da tsarkakken zaɓe na gaskiya da adalci.

Sanarwar da Kwamishinan ya fitar ta ƙara da cewa, dokar ta shafi dukkan ƙananan hukumomin jihar 44 da gundumomin zaɓe 484 da ke faɗin jihar.

Talla

Sanya dokar dai na zuwa ne ƙasa da sa’o’i 24 gabanin zaɓen ƙananan hukumomin Kano da zai gudana a gobe Asabar, 26 ga watan Oktoba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hakikanin halin da gwamnan Katsina yake ciki, bayan wani hatsari

  Rahotanni daga Katsina na cewa gwamnan jihar Katsina Dikko...

Zargin almundahana: ICPC ku fita daga harkokin Siyasar Kano – Kungiyar Ma’aikatan KANSIEC

Daga Hafsat Abdullahi Darmanawa   Kungiyar ma'akatan wucin gadi da suka...

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...